Posts

Showing posts from June, 2018
Write Your First Flutter App, part 1 http://flip.it/aX3hD-

Mulkin mace a mahangar islam

Asslamu alaikum. Zance mafi inganci kan shugabancin mace a musulunci . Godiya ta tabbata ga Allah, tsira da aminci su tabbata ga shubanmu Muhammad da alayensa da sahabbansa, damu gaba daya. Amma bayan haka: Lokaci yayi – a ganina – da ya kamata in fadakar da yan’uwa kan  mas’alar nan da ake ta cece-kuce kanta, wato mas’alar shugabancin mace a musulunci .wato ya hallatta mace tayi shugabanci kan mutane a musulunce ko kuwa ? A dan karamin bincike da nayi – a gurguje -kan wannan mas’alar, na fahimci maluma sun kasu kashi biyu, masu halatta haka, da masu haramta hakan. Sudai masu haramta hakan suna dogarone da wani hadisi da Imam Bukhari ya ruwaito mai lamba 7099, daga Abi Bakrah, inda yake cewa : manzon Allah yace: لَنْ يُفْلِحَ قَوْمٌ وَلَّوْا أَمْرَهُمْ امْرَأَةً Ma’ana: Duk mutanen da suka baiwa mace mulki akansu bazasu ci nasara ba. Su kuwa masu halatta hakan, cewa suke, ai wannan maganar labarine irin na annabta da manzon Allah ke badawa, ba hukunci bane balle a fake dashi a